Allah ya yi wa tsohon gwamnan Gombe kuma Sarkin Billiri Dr Abdu Buba rasuwa
- Tsohon gwamnan Gombe, Ibrahim Dankwambo ya yi wa iyalan Sarkin da al'ummar jihar ta'aziyya
- Ɗankwambo ya ce rasuwar Sarkin babban rashi ne ya kuma yi addu'ar Allah ya gafarta masa Tsohon gwamnan Jihar Gombe, kuma jigo a jam'iyyar Peoples Democratic Party, ya sanar da rasuwar Sarkin mai daraja ta farko cikin wani sako da ya wallafa a Twitter.
Ya rubuta; "Ni da iyalaina na son miƙa sakon ta'aziyyar mu ga mutanen Gombe game da rasuwar Mai Martaba, Dr. Abdu Buba Maisheru II (Mai Tangale) Sarkin Billiri. Rasuwarsa ya zo mana a matsayin abun mai firgici amma muna addu'ar Allah ya jiƙansa,"


No comments:
Post a Comment