Kungiyar wace ta tattara gwamnoni masu ci a yanzu da kuma tsofaffin gwamnoni, suna so Makarfi ya zamo dan takarar shugabancin kasa na PDP. An kuma tattaro cewa yayinda PDP ta mika tikitin dan takarar shugabancin 2019 ga arewa, shugabancin jam’iyyar zai koma kudu maso yamma.
Wata majiya tace yan jam’iyyar da dama sun amince da cewa tsohon gwamnan na jihar Kaduna baida wani nauyin siyasa sannan kuma cewa hakan zai basu damar yakin neman zabe cikin sauki da suka nasarar jam’iyyar a 2019. Koda dai Makarfi bai nuna ra’ayin tsayawa takara a zabe mai zuwa ba, maganganu sun nuna cewa zai yi nasara a kan shugaba Muhammadu Buhari. A baya Hausazone.com ta kawo cewa gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya kaddamar da ra’ayinsa na tsayawa takarar shugabancin kasa a 2019.
No comments:
Post a Comment