Wednesday, February 17, 2021

Sanusi ya bukaci gwamnati ta kayyadewa 'yan Najeriya yawan iyalin da za su haifa

 Sanusi ya bukaci gwamnati ta kayyadewa 'yan Najeriya yawan iyalin da za su haifa 




- Tubabben sarkin Kano, Sanusi II ya bukaci gwamnati da ta saka dokar kayyade yawan iyali


 - Tsohon shugaban babban bankin ya ce hakan ne kawai zai kawo daidaituwar yawan 'yan Najeriya 


- Muhammadu Sanusi ya ce ba Musulunci bane haifar yaran da ba za a iya kula da su da kyau ba Tsohon sarkin Kano, Muhammad Sanusi II yayi kira ga gwamnati da ta saka tsauraran dokoki da za su daidaita hauhawar yawan jama'a a kasar nan. 


Sanusi wanda yayi magana a ranar Laraba yayin wani taro a Legas, ya ce ya dace jama'a su dinga haifar yaran da za su iya kula da su, Daily Trust ta wallafa. 


Kamar yadda tsohon gwamnan babban bankin Najeriya yace, abubuwan da ke bayyana a halin yanzu sun nuna cewa gwamnati ba za ta iya samar da dukkan ababen more rayuwa da ake bukata ba. 


Sanusi ya kushe yadda ake haihuwa a kasar nan ba tare da karfin kula da yaran ba, wanda yace hakan ba daidai bane ko a addinin Musulunci. Ya ce: "Yadda jama'a ke auren duk yawan matan da suke so ba tare da wata dokar da ta gindaya yawan yaran da za a haifa ba bai dace ba ko a Musulunci. "Ban san dalili ba amma akwai doka a Musulunci da ta hana tara iyali ba tare da kayyade su ba. Babu wani tabbacin cewa za a iya kula dasu ba tare da an yi watsi da dawainiyarsu ba." 


A wani labari na daban, tsohon shugaban majalisar dattawa, Dr Bukola Saraki ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ba zai samu damar tsayawa takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar APC ba a zaben shugaban kasa 2023. 


No comments:

Post a Comment

Pages