Gwamnatin jihar Kano tana neman Likitocin da za ta ɗauka aiki ruwa a jallo
Ma’aikatar Lafiya ta jihar Kano ta sanar da shirin ta na neman Likitocin da za su yi aiki da ɓangaren kiwon lafiya a matakin farko na jihar wato Primary Health Care.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta wallafa a shafukan ta na facebook da tuwita.
Haka kuma ma’aikatar ta bayar da adereshin da ga duk mai buƙata zai iya tura cikakken bayanin sa tare da takardunsa kamar haka:
sphcmbrecruitment@gmail.com

No comments:
Post a Comment