Da Duminsa: Bayan Wanke wanda yawa Allah batanci da Kotu ta yi a Kano, Turawa sun tafi dashi kasarsu
Matashi Umar Farouk da a baya kotu ta yankewa hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari bayan samunsa da kalaman Batanci ga Allah ya tafi kasar waje.
Shafin Kasar Porland na Auschwitz-Birkenau Memorial and Museum ya bayyana cewa an fitar da Farouk daga Najeriya ne saboda yana ci gaba da samun barazana daga wasu Mutane.
A shekarar 2020 ne dai kotun ta daureshi bayan an sameshi da laifin kalaman batanci ga Allah a yayin da yake Chatting da wani abokinsa. Matashin a wancan lokacin yana da shekaru 13 ne.
A watan Janairu ne dai wani lauya daga jihar Legas, Kola Alapini ya daukaka kara kan Umar kuma aka wankesa daga laifin.
Wakilin waccan cibiya ta kasar Poland, Piotr Cywinski ya bayyana cewa zasu samarwa Umar Sabuwar Rayuwa da daukar Nauyin karatunsa da biyan Lauyan da ya tsaya masa, ta hanyar neman Tallafi.
Saidai be bayyana a inda zasu ajiye matashin ba dan tsaro

No comments:
Post a Comment