Monday, October 2, 2017

Aiki dai! Gwamnatin Buhari ta shirya tsaf don fara aikin shimfida hanyoyin jiragen kasa 10


Gwamnatin tarayya a karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta gama shiri tsaf domin fara shinfida hanyoyin jiragen kasa akalla kimanin guda goma sabbi fil nan ba da dadewa ba a dukkan fadin kasar nan. Mun samu dai cewa wannan na kunshe ne a cikin wani sabon daftarin aiki na hukumar da ke kula da harkokin sufuri na jiragen kasa ta gwamnatin tarayya.

NAIJ.com ta samu kuma haka zalika cewa jumillar tsayin hanyoyin idan aka kammala su zai kama kimanin ma'aunin tsawo na kilomita 3,421. Haka ma dai kamar dai yadda daftarin ya kunsa, hanyoyin jiragen kasar za su bi ne ta jihohin Lagos, Oyo, Osun, Ogun, Benin, Abuja, Kogi, Onitsha da Sokoto.
Kamar kuma yadda muka samu shine cewa hanyoyin da za'a fara shinfidawar sune na Lagos-Sagamu-Ijebu Ode-Ore-Benin City; sai Lagos-Ibadan-Osogbo-Baro-Abuja; sai kuma Ajaokuta (Eganyin)-Obajana-Jakura-Baro-Siraj-Abuja da kuma Ajaokuta zuwa Otukpo. Haka ma dai akwai Zaria-Kaura Namoda-Sokoto-Ileila-Birnin Koni a Niger Republic da dai sauran su.

No comments:

Post a Comment

Pages