Ta ce ta so ta bayyana a kotun Najeriya don kare laifin cin hanci da aka yi zargi ta aikata na naira miliyan 450, inda aka ambaci sunanta.
Amma Malami ya ce gwamnatin Birtaniya ta riga ta dauki matakan da ta dace kan batun. Ministan ya ce idan gwamnatin tarayya ta ga dalilin da zai sa a dawo da tsohon ministan, ba za ta jinkirta yin haka ba. Malami ya ce gwamnati ta na kokari wajen magance cin hanci da rashawa a Najeriya da waje.
No comments:
Post a Comment