Wata majiya mai karfi ta shaida ma jaridar The Nation cewa “Dangane da dokokin mallaka, mun samu cikakken bayanai kan wasu yan Najeriya dake kasar Dubai, haka zalika mun samu wani jerin sunayen yan Najeriya da muke bincika a yanzu. An samu wannan bayanai ne bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rattafa hannu kan yarjejeniyar kwato arzikin gwamnati da aka sace,a satin data gabata..” Inji majiyar. NAIJ ta ruwaito shugaban kasa Buhari ya rattafa hannu kan yarjejeniyar ne da nufin zaburar da hukumomin yaki da rashawa na Najeriya tare da samun goyon bayan kasar Dubai wajen dawo da arzikin kasa da aka sace aka kai can.
No comments:
Post a Comment