Gwamnan jihar Rivers, Nyeson Wike ya bayyana cewa shugabannin PDP na Arewa ne suka yaudari Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan inda suka samar da kafar da Shugaba Buhari ya samu nasarar lashe zaben 2015. Ya ce tsohon Shugaban PDP na kasa, Adamu Mu'azu tare da hadin bakin wasu gwamnoni da ministoci daga Arewa sun rika yi wa Jonathan karya ta hanyar ba shi tabbacin cin zabe amma kuma daga bayan fage sun rika yi wa APC aiki. Ya kara da cewa a halin yanzu PDP na Zawarcin Tsohon Shugaban Kasa, Cif Olusegun Obasonjo da Tsohon Mataimakinsa, Atiku Abubakar da kuma tsohon Gwamnan Legas kuma jigo a APC, Bola Ahmed Tinibu.
No comments:
Post a Comment