Ibrahim, wanda shine yaro daya tilo da Allah ya baiwa majinyacin, yace “Mahaifina na fama da jinya sosai, sai dai babu wani mai bamu taimako, har da masana’antar Kannywood kuwa.”
Ibrahim ya kara da cewa a yanzu haka ciwon mahaifinsa ya kai matsayin a yi masa wankin koda. Amma Ibrahim din yace a kwanaki Ali Nuhu ya basu N25,000, yayin da Sadik Sani ya basu N35,000, bayansu babu wanda ya taimake su a cikin yan Fim. Daga bangaren sauran jama’a kuwa, Ibrahim yace Hajiya Zainab Ziya’u ta basu taimakon N220,000, sai kuma kanwar Ummi Zee Zee, Haseena data basu N300,000, kamar yadda majiyar mu ta ruwaito.
No comments:
Post a Comment